Nnamdi Kanu na da ƙoshin lafiyar fuskantar shari’a – Ƙungiyar Likitoci

0
100

Ƙungiyar Likitocin Najeriya (NMA) ta bayyana cewa lafiyar Nnamdi Kanu ba ta kai ga barazana ga rayuwarsa ba, don haka yana da ƙoshin lafiya don ci gaba da fuskantar shari’a.

A ranar 26 ga Satumba, Mai shari’a James Omotosho ya umarci shugaban NMA da ya kafa tawagar bincike domin tantance halin lafiyar Kanu, don ganin ko yanayin sa na bukatar a fita dashi a duba lafiyar sa.

Wannan umarni na kotu ya biyo bayan buƙatar da aka shigar don a tura shugaban haramtacciyar ƙungiyar IPOB ɗin daga hannun hukumar DSS zuwa Asibitin Kasa da ke Abuja domin kula da lafiyarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here