PDP ta ɗage babban taron ta na kwamitin zartaswa

0
8

Jam’iyyar PDP ta sanar da dage babban taron kwamitin zartarwarta da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 15 ga Oktoba, 2025.

A cewar wata sanarwa da jam’iyyar ta wallafa a shafinta na X, tace an ɗauki wannan mataki ne bayan wani taron gaggawa da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya gudanar a Abuja a ranar Litinin.

Jam’iyyar ta bayyana cewa za ta sanar da sabuwar rana a nan gaba, tare da roƙon mambobinta da su jira sabon jadawalin taron.

PDP na fuskantar ƙalubale a cikin gida sakamakon yawaitar ficewar manyan mambobinta zuwa jam’iyyar APC mai mulki, ciki har da jita-jitar cewa wasu daga cikin gwamnoninta biyu ma na shirin komawa APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here