Ya kamata a binciki takardun kammala karatun ministocin Tinubu–Atiku

0
16

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da mayar da jabun takardun kammala karatu da karya hanyar mulki a Najeriya.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Atiku ya ce murabus ɗin ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, saboda zargin jabun takardu, ya nuna “rashin ɗabi’a mai kyau” a cikin gwamnatin Tinubu.

Ya kuma soki jami’an tsaro na farin e DSS da gazawa wajen tantance jami’an gwamnati, yana cewa “hukumar da ta hana El-Rufai mukami ce ta amince da Uche Nnaji.”

Atiku ya ƙara da cewa rikicin takardun shugaban ƙasa Tinubu ya gurbata tsarin mulki, inda ya ce:

> “Idan wanda ke mulki yana da matsalar gaskiya, to karya ce zata zama al’ada a gwamnatin sa.”

Ya bukaci a gudanar da bincike kan takardun dukkan ministoci da shugaban ƙasa, yana mai cewa:

> “Sai an dawo da gaskiya cikin gwamnati sannan Najeriya za ta fita daga halin lalacewa.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here