Tattara haraji ba zai hana ciyo bashin ƙasashen waje ba–Gwamnatin tarayya

0
98
Bola Tinubu
Bola Tinubu

Shugaban Hukumar Tattara Haraji ta Ƙasa (FIRS), Zacch Adedeji, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga a watannin baya-bayan nan.

Adedeji ya ce ɗaukar bashi ba alamar rauni ba ne, illa kawai wani ɓangare na dabarun tattalin arzikin ƙasa. Ya bayyana cewa a watan Satumba 2025, FIRS ta tara harajin da ya kai Naira tiriliyan 3.64, wanda ya ninka da kashi 411 cikin ɗari daga Naira biliyan 711 da aka tara a Mayu 2023.

Sai dai wannan na zuwa ne bayan kusan wata biyu da Shugaba Bola Tinubu ya nemi aron $21.5bn daga kasashen waje, ciki har da bashi na $2bn da kuma N757.98bn don biyan bashin fansho.

A baya-bayan nan, gwamnatin Tinubu ta sha suka daga masana da ‘yan ƙasa kan yadda take ta dogaro da bashi duk da samun karuwar kudaden shiga.


LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here