Sudan Ta Lallasa Najeriya 4-0 a Gasar CHAN

0
8

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Sudan ta fitar da Nijeriya daga gasar CHAN bayan ta lallasa ta da ci 4-0 a wasan maraicen Talata, wanda ake bugawa tsakanin ‘yan wasan da ke taka leda a ƙasashen Afirka kawai.

Wasan shi ne na biyu da Nijeriya ta buga a Rukunin D, wanda aka yi a Filin Wasa na Amaan da ke birnin Zanzibar, Tanzania.

A makon jiya, Senegal ma ta doke Nijeriya da ci 1-0 a gasar ta CHAN 2024.

Sakamakon wannan nasara, Sudan na gab da tsallakewa zuwa mataki na gaba a gasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here