Zan Yanke Hukunci Kan Shiga Yaƙin Isra’ila da Iran Nan da Mako Biyu–Trump

0
24

Zan Yanke Hukunci Kan Shiga Yaƙin Isra’ila da Iran Nan da Mako Biyu–Trump

Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa cikin mako biyu masu zuwa zai yanke shawara kan ko zai shiga yaƙin da Isra’ila ke yi da Iran, ko kuma akasin haka.

A cikin wata sanarwa da sakatariyar yaɗa labaran fadar White House ta karanto, Shugaban ya ce akwai yiwuwar a warware rikicin ta hanyar zaman teburin sulhu.

Kafin fitowar wannan sanarwar, mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Saeed Khatibzadeh, ya shaida wa BBC cewa Iran ba ta da wata matsala da tattaunawar diflomasiyya, muddin aka dakatar da kai mata hare-haren bama-bamai.

Ya ce, duk da cewa Iran a shirye take ta shiga tattaunawa cikin lumana, hakan ba yana nufin za ta sassauta matsayinta game da Isra’ila ba.

Ya kuma gargaɗi cewa dukkan yankin gabas ta tsakiya zai shiga cikin rikici mai tsanani idan har Amurka ta ƙudiri aniyar shiga yaƙin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here