Mun adana kudade masu yawa saboda cire tallafin fetur—Gwamnatin tarayya

0
98

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa cire tallafin man fetur da Shugaba Bola Tinubu ya aiwatar ya kawo ƙarshen wata babbar asarar kuɗi da ta ci wa Najeriya sama da dala biliyan 84, kuma ya bai wa gwamnatin damar kammala manyan ayyukan tituna guda 40 a fadin kasar nan a cikin shekaru biyu.

Bayanin hakan na cikin wata takardar bayanin manufofin gwamnati da Hukumar Wayar da Kai ta Kasa (NOA) ta fitar mai taken “Bayan Shekaru Biyu, Muhimman Fa’idodin Cire Tallafin Fetur.

A cewar NOA, cire tallafin da aka yi tun daga ranar 29 ga Mayu, 2023 ya ceci Najeriya daga tabarbarewar tattalin arziki, ya kuma bai wa gwamnatin Tinubu damar biyan basussukan daya gada da kuma daidaita kasafin kudi a matakin jihohi.

Tsawon shekaru da dama, musamman tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya, tsarin tallafin man fetur ya kasance babban kalubale ga Gwamnatin Tarayya. Duk da kokarin gwamnatocin baya na shawo kan lamarin, tsarin ya ci gaba da haddasa asara ga tattalin arzikin kasa. A shekarar 2022 kadai, kasafin kudin tallafi ya karu da kashi 700% zuwa naira tiriliyan 4 mafi girma a tarihin Najeriya.

An kiyasta cewa daga shekarar 2005 zuwa 2022, an kashe dala biliyan 84.39 wajen tallafin fetur, inda hakan ya lashe sama da kashi 70 cikin 100 na kudaden shiga da gwamnati za ta iya samu, lamarin da ya jefa kasar cikin halin rashin kudi. Amma da aka yanke shawarar cire tallafin, yanzu Najeriya tana ajiye biliyoyin daloli kuma tana amfani da su wajen samar da ababen more rayuwa.

A cewar hukumar NOA, furucin da Shugaba Tinubu ya yi ranar farko da ya hau kujerar mulki, inda ya ce “Tallafi ya tafi”, ya bude kofar gyare-gyare masu wahala amma masu tasiri, wanda suka kawo inganta ribar kudade a fannoni daban-daban.

Daya daga cikin manyan tasirin cire tallafin, kamar yadda NOA ta bayyana, shi ne kara darajar kasafin kudin gwamnatocin jihohi.

Har ila yau, NOA ta bayyana cewa kudin da aka ajiye daga cire tallafin ya bawa gwamnati damar biyan bashin dala biliyan 7 da ake bin ta na kudin musaya (Forex) da kamfanonin waje suka dade suna bin gwamnatin tarayya lamarin da ya sa Najeriya ta zama ta farko a duniya wajen bashi a bangaren canjin kudi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here