Zamu kawar da gwamnatin Tinubu a 2027–Atiku, El-Rufa’i da Obi

0
143

Manyan jiga-jigan ’yan adawar kasar nan guda uku, da suka haɗar da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, da tsoffin gwamnonin Kaduna da Rivers, Nasir El-Rufai da Rotimi Amaechi sun ƙalubalanci gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu kan tabarbarewar tsaro, yunwa da yawaitar talauci a Najeriya, inda suka sha alwashin kawar da Tinubu a shekara ta 2027.

Sun bayyana hakan ne a ƙarshen mako yayin wani taron da aka gudanar na bikin cika shekara 60 da haihuwar Rotimi Amaechi.

Ƴan adawar sun gwamnatin tarayya tana yin amfani da talauci a matsayin makamin da take yaƙar yan Najeriya.

Atiku Abubakar, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya zargi gwamnatin Tinubu da yin amfani da talauci a matsayin wata hanya ta cimma manufofin siyasa da sarrafa al’umma.

Dalilin hadin kanmu shi ne hana gwamnatin Tinubu, ci gaba da amfani da talauci wajen danniya da mulkin zalunci, inji Atiku

Ya kara da cewa gwamnatin ta gaza cika alkawuran data ɗauka, kuma tana amfani da wahalar rayuwa a matsayin  siyasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here