An kama mai garkuwa da mutane zai tafi aikin hajji

0
200

An kama mai garkuwa da mutane zai tafi aikin hajji 

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an tsaro sun kama wani mutum da aka jima ana nema bisa zargin garkuwa da mutane, inda a yanzu aka same shi a sansanin alhazai na birnin tarayya Abuja.

Wata majiya daga sansanin itace ta tabbatar da hakan ga jaridar Daily trust.

Majiyar tace an samu nasarar kama ɗan ta’addan a yau Lahadi, yayin tantance maniyyatan da za su tafi ƙasa mai tsarki domin yin aikin hajjin bana.

Ɗan garkuwar mai suna Yahaya Zango, ya kasance mazaunin Paikon-Kore, ne dake karamar hukumar Gwagwalada da a Abuja.

Kamar yadda aka samu bayanai jami’an tsaro sun dade suna nemansa bisa zargin hannu a wasu hare-hare da garkuwa da mutane.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here