Kotu ta bayar da belin Farfesa Usman Yusuf

0
31

Kotu ta bayar da belin Farfesa Usman Yusuf bayan shafe kwanaki 24 a hannun jami‘an tsaro bisa zargen-zargen aikata ba daidai ba da hukumar EFCC.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC, ce ta kama Farfesan kwanakin baya a gidan sa dake Abuja, wanda bayan dan lokaci ta gurfanar da shi a gaban kotu bisa zargin sa da aikata laifi a wata kungiya.

Farfesa Usman Yusuf, ya kasance daya daga cikin masu kalubalantar manufofin gwamnatiin Tinubu, da ake ganin hakan na daga cikin abubuwan da suka kara sanyawa aka kama shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here