Tinubu Ya Naɗa Sabon Shugaban Hukumar NERC

0
11

 

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake fasalin Hukumar Kula da Harkokin Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC), da mambobin hukumar a ranar 16 ga Disamba, 2025.

A cikin sanarwar da mai bawa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya buƙaci sabbin mambobin NERC su ƙarfafa sauye-sauyen da ake yi a ɓangaren wutar lantarki, bisa tanadin Dokar Wutar Lantarki ta 2023.

Sabbin mambobin kwamitin NERC sun haɗa da:

Dr. Mulisiu Olalekan Oseni — Shugaba

Dr. Yusuf Ali — Mataimakin Shugaba

Nathan Rogers Shatti — Kwamishina

Dafe Akpeneye — Kwamishina

Aisha Mahmud Kanti Bello — Kwamishina

Dr. Chidi Ike — Kwamishina

Dr. Fouad Animashaun — Kwamishina

Nadin Dr. Oseni ya fara aiki daga 1 ga Disamba, 2025, kuma zai cika wa’adin shekaru goma a hukumar, kamar yadda doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here