Tinubu ya turawa majalisar dattawa sunan mutanen da zai naɗa a matsayin jakadu

0
9

Tinubu ya turawa majalisar dattawa sunan mutanen da zai naɗa a matsayin jakadu

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya aika da jerin sunayen mutane uku da yake son a tabbatar wa a matsayin jakadu zuwa Majalisar Dattawa.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya karanta sunayen a zaman majalisar na ranar Laraba.

Masu jiran tabbatarwar su ne:

  • Kayode Are
  • Aminu Dalhatu
  • Ayodele Oke

Akpabio ya ce wannan jerin farko ne, yana mai cewa akwai yiwuwar ƙarin sunaye su biyo baya.

A halin yanzu ba a fitar da cikakken bayani kan inda za a tura su ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here