Atiku Abubakar ya bayyana lokacin da zai koma jam’iyyar ADC

0
8

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, yana dab da bayyana komawar sa jam’iyyar ADC a hukuman ce a gobe Litinin, matakin da ake ganin zai iya sauya taswirar siyasar Najeriya nan gaba kaɗan.

Yayin da yake jawabi ga magoya baya da jiga-jigan jam’iyyar ADC a Jihar Adamawa, Atiku ya bayyana cewa zai yi rajista da jam’iyyar a ranar Litinin.

Ana sa ran wannan sauyin zai haifar da bayyana mabanbantan ra’ayi a jam’iyyun siyasa, musamman duba da tasirin Atiku a arewa da kuma shirin jam’iyyar ADC na faɗaɗa karfinta a matakin ƙasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here