Natasha ta zargi Akpabio da bayar da umurnin ƙwace mata fasfo

0
14

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan daga yankin Kogi ta Tsakiya ta zargi shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, da bayar da umarni ga shugaban hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) a kan ƙwace mata fasfo a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

A cikin wani bidiyo da ta wallafa a yanar gizo, Natasha ta bayyana cewa wannan umarni ne ya hana ta tafiya ƙasashen waje.

Cikin fushi sanatar ta bayyana cewa kamar yadda aka yi mata makamancin haka a baya, a yanzu ma an ƙwace fasfo ɗin ta duk da cewa bata aikata laifin komai ba, tana mai cewa shugaban majalisar dattawa ne ke da alhakin wannan musgunawa da ta fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here