Tinubu ya miƙa wa majalisar dattawa bukata a kan sabbin hafsoshin tsaro

0
4

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika wa majalisar dattawa da buƙatar tantancewa da tabbatar da sabbin hafsoshin tsaro da ya nada kwanan nan.

An karanta wasikar shugaban ƙasar a zauren majalisar ranar Talata ta hannun shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.

Sabbin shugabannin da aka mika sunayensu sun haɗa da:

Janar Olufemi Oluyede – Babban Hafsan Tsaro (CDS)

Manjo Janar Waheedi Shaibu – Hafsan Sojan Kasa (COAS)

Rear Admiral Idi Abbas – Hafsan Sojan Ruwa (CNS)

Air Vice Marshal Kennedy Aneke – Hafsan Sojan Sama (CAS)

Manjo Janar Emmanuel Undiendeye – Hafsan Leken Asiri na Tsaro (CDI)

Bayan karanta wasikar, Akpabio ya umurci cewa a mika sunayen waɗanda aka zaɓa ga Ɗaukacin Kwamitin Majalisar domin gudanar da tantancewa da tabbatarwa a mako mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here