Tinubu Ya Rantsar Da Sabon Shugaban INEC

0
9

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Farfesa Joash Amupitan (SAN) a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

An gudanar da taron rantsuwar ne a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, tare da halartar manyan jami’an gwamnati da shugabannin majalisar dokoki.

Farfesa Amupitan, ɗan asalin ƙaramar hukumar Ijumu a Jihar Kogi, ya gaji Farfesa Mahmood Yakubu, wanda wa’adinsa ya ƙare.

An amince da nadinsa ne bayan majalisar koli ta amince da sunansa kuma majalisar dattawa ta tabbatar da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here