Kotu ta yanke hukunci ga matasan da suka kashe malamin jami’ar Northwest Kano

0
21

Babbar kotun jihar Kano ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga Aliyu Hussaini da Amir Zakariyya bisa laifin kashe malamin Jami’ar Northwest Kano, Buhari Imam, a shekarar 2016.

Mai shari’a Fatima Adamu ta ce kotu ta tabbatar da cewa sun kai wa malamin hari a gidansa a Sheka, suka sace wayarsa sannan suka soka masa wuka har ya mutu.

Kotun ta yanke musu shekaru biyar a gidan yari kan hada baki, shekaru goma kan fashi da makami, sannan hukuncin kisa ta hanyar rataya kan kisan kai.

Lauyan gwamnati, Lamido Abba-Sorondinki, ya tabbatar da cewa hujjojin gwamnati sun tabbatar da laifin waɗanda ake zargi, yayin da kotu ta ki amincewa da rokon sassauci daga lauyansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here