Gwamnatin Tarayya ta gargadi kungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa ASUU, cewa za ta aiwatar da dokar ba aiki, ba albashi idan malaman suka shiga yajin aiki.
A wata sanarwa da mai magana da yawun Ma’aikatar Ilimi, Folasade Boriowo, ta fitar a daren Lahadi, gwamnati ta nuna rashin jin daɗin yadda ASUU ta ƙi bata haɗin kai, duk da tattaunawar da ake yi domin kauce wa yajin aikin da suke shirin shiga a ranar Litinin.