Tinubu ya gabatar da sunan sabon shugaban hukumar zaɓe INEC

0
75
Tinubu
Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai gabatar da sunayen waɗanda zai iya nada wa matsayin shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a zaman Majalisar Koli ta Ƙasa da ake gudanarwa a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Zaman majalisar, wanda aka fara da misalin ƙarfe 1:29 na rana a ranar Alhamis, 9 ga Oktoba, 2025, ya samu halartar manyan jagororin ƙasa da tsofaffin shugabanni.

Rahotanni daga jaridar The Punch sun bayyana cewa shugaban ƙasa ya gabatar da mutane uku domin tantancewa a matsayin magajin Farfesa Mahmood Yakubu wanda wa’adinsa ya ƙare. 

Mutanen sune:

Farfesa Joash Amupitan,

Mai shari’a Abdullahi Mohammed Liman,

Da Farfesa Lai Olurede.

Dukkan masu neman wannan mukami ƙwararru ne a fannin shari’a da ilimi, kuma ana sa ran majalisar za ta tantance su kafin a yanke hukunci na ƙarshe kan wanda zai zama sabon shugaban INEC.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan yadda za a inganta tsarin zaɓe a Najeriya kafin babban zaɓen da ke tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here