Za’a hana wasu ƴan Najeriya mallakar fasfo na tsawon shekaru 10

0
41

Majalisar Dattawa ta amince da dokar da za ta hana ɗan Najeriya da aka tabbatar da laifi a ƙasashen waje mallakar fasfo na tsawon shekaru goma.

An amince da wannan kudiri ne a zaman majalisar na ranar Talata, a matsayin mataki na dakile ayyukan da ke bata sunan Najeriya a kasashen ƙetare.

Wannan dokar na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na inganta ɗabi’un ‘yan ƙasa da kuma kare mutuncin Najeriya a idon duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here