Kano da wasu jihohi 10 zasu fuskanci ruwan sama mai ƙarfi

0
41

Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗi cewa jihohi 11 za su iya fuskantar ruwan sama mai ƙarfi wanda ka iya jawo ambaliyar ruwa daga yau Lahadi zuwa Alhamis.

A cewar sanarwar da Ma’aikatar Muhalli ta fitar ta hannun Cibiyar Fadakar da Ambaliya ta Ƙasa (National Flood Early Warning Centre), jihohin da abin zai shafa sun haɗa da:

Adamawa: Ganye, Natubi

Benue: Abinsi, Agyo, Gogo, Ito, Makurdi, Udoma, Ukpiam

Nasarawa: Agima, Rukubi, Odogbo

Taraba: Beli, Serti, Donga

Delta: Umugboma, Umukwata, Abraka, Aboh, Okpo-Krika

Niger: Rijau

Kebbi: Ribah

Kano: Gwarzo, Karaye

Katsina: Jibia

Sokoto: Makira

Zamfara: Kaura Namoda, Shinkafi, Maradun, Gusau, Anka, Bungudu

An ba da shawarar cewa al’ummar da ke kusa da koguna su gaggauta barin wuraren don guje wa hadurra.

Haka kuma, an bukaci gwamnatocin jihohi da hukumomi masu ruwa da tsaki su ɗauki matakan gaggawa don rage illar da hakan zai iya haifarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here