Adadin ƙungiyoyin ƴan ta’addan arewa, da dalilin kafuwar su a yankin

0
33

Fiye da shekara 15 kenan yankin arewacin Najeriya yana fama da hare-haren kungiyoyin masu ɗauke da makamai. Wadannan kungiyoyi sun jima suna kai hare-hare kan fararen hula da jami’an tsaro tare da sace mutane domin neman kuɗin fansa, lamarin da ya tilasta wa miliyoyin mutane barin muhallansu.

Hare-haren sun fara ƙara tsanani tun daga shekarar 2008, lokacin da ƙungiyar Boko Haram ta fara kai farmaki a jihar Borno. Daga baya wasu sabbin ƙungiyoyi suka fito, suna bazuwa a jihohi daban-daban na arewacin ƙasar.

A ƙasa akwai jerin fitattun kungiyoyi da suka fi addabar arewa:

1. Boko Haram

An kafa ta a 2002 a jihohin Borno da Yobe.

Ta fara da wa’azi kafin komawa amfani da makamai.

Ta shahara bayan kisan gilla da sace daliban Chibok a 2014.

Shugabanninta sun haɗa da Muhammad Yusuf da kuma Abubakar Shekau.

2. ISWAP (Islamic State West Africa Province)

Ta fito a 2016 bayan ta balle daga Boko Haram.

Jagoranta na farko shi ne Abu Mus’ab al-Barnawi, ɗan marigayi Muhammad Yusuf.

3. Ansaru

An kafa ta a 2012 a jihohin Kaduna da Kano.

Ana danganta ta da ƙungiyar al-Qaeda.

Fitaccen harinta shi ne kai farmaki gidan yarin Kuje a 2022.

4. Ƙungiyar Lakurawa

An fara samun ta a 2018 a jihohin Sokoto da Kebbi.

A farkon lokaci an ɗauke ta tamkar ƙungiyar kariya daga ‘yan fashi, daga baya ta shiga tsarin ta’addanci.

Ana danganta ta da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi a Sahel.

5. Ƙungiyar Ta’addan Tsakiyar Najeriya

Ta bayyana a 2024 a jihohin Neja da Kwara.

Ana ce tana da alaƙa da wasu al’ummu a Jamhuriyar Benin.

Ta fi amfani da dabarun satar shanu, harajin ƙauyuka, da kuma kai hare-hare.

Ana danganta ta da Ansaru da al-Qaeda.

6. Ƴan Bindiga a Zamfara da Arewa maso Yamma

Sun fara bayyana tun 2010 a Zamfara kafin su watsu zuwa wasu jihohi.

Sun yi suna wajen sace mutane, kwace wuraren kiwo, da kuma kashe-kashe.

Daga cikin shugabanninsu akwai Bello Turji, Ado Aliero, da Dogo Giɗe.

Wasu kuma sun mutu kamar Buharin Daji da Halilou Sububu.

Me ya haddasa yawaitar kungiyoyin ?

Masana tsaro na ganin matsalar tana da alaƙa da:

Rashin aikin yi,

Karancin ilimi,

Da sauyin yanayi da ya shafi noma da kiwo.

Duk da cewa a kudu ma akwai matsalar ‘yan bindiga, amma a arewa ta fi muni saboda yawan kungiyoyi da tsananin hare-hare.

Majiya: Dakta Kabiru Adamu Shugaban Kamfanin Beacon Security mai nazarin tsaro a yanken Sahel, kamar yadda BBC Hausa, ta wallafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here