PDP zata bawa ɗan kudu takarar shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027

0
8

Jam’iyyar PDP ta amince ta bayar da tikitin takarar shugabancin kasa na shekarar 2027 zuwa yankin Kudu.

Shugabannin jam’iyyar sun dauki wannan mataki ne a taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da aka gudanar a ofishin jam’iyyar dake Abuja ranar Litinin.

Wannan mataki na iya sauya taswirar siyasar PDP, inda ake sa ran manyan ‘yan siyasar kudu za su fara shiri domin neman tikitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here