Godswill Akpabio, ya karyata jita-jitar rashin lafiyarsa

0
1

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya musanta jita-jitar da ke yawo a shafukan sada zumunta cewa yana fama da rashin lafiya mai tsanani a birnin London.

Akpabio ya sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da misalin ƙarfe 4 na asubahin ranar Litinin, bayan dawowa daga London. An tarbe shi a sashen shugabanni na filin jirgin ta hannun wasu sanatoci, hadimai da magoya baya.

Rahotanni a kafafen sada zumunta sun ruwaito cewa shugaban majalisar dattawan na kwance a asibiti, lamarin da ya bayyana a matsayin ƙarya tsagwaronta.

Lafiyata ƙalau take. Na tsaya a London ne kawai don ɗan hutu na ɗan lokaci,” in ji shi yayin da yake zantawa da manema labarai a filin jirgin.

Tun kafin wannan hutu, Akpabio ya halarci taron shugabannin majalisun dokoki na duniya karo na shida a Geneva, Switzerland, daga ranar 29 zuwa 31 ga watan Yuli.

LEAVE A REPLY

Logged in as Ismail Ishaq-Ibrahim. Log out?

Please enter your comment!