An ɗaura auren Jaruma Rahama Sadau

0
17

An ɗaura auren fitacciyar jarumar fina-finan Najeriya, Rahma Sadau, da Alhaji Ibrahim Garba a ranar Asabar a Kaduna.

An gudanar da ɗaurin auren ne misalin ƙarfe 11 na safe a Masallacin Atiku Auwal da ke Unguwar Rimi, inda ‘yan uwa da abokan arziki kaɗan suka halarci taron.

An bayyana Naira dubu ɗari 3 a matsayin sadakin aurenta.

Majiyoyi sun ce jarumar ta zaɓi yin bikin a sirrance.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here