Tattalin arzikin Najeriya zai ƙara haɓɓaka a 2025 zuwa 2026–IMF

0
17

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya fitar da sabon hasashen da ke nuna ƙaruwar ci gaban tattalin arzikin Najeriya a shekarar 2025 da 2026.

A sabon rahoton da IMF ya fitar a watan Yuli, ta ƙiyasta cewa tattalin arzikin Najeriya zai bunƙasa da kashi 3.4 cikin 100 a shekarar 2025, wanda ya fi hasashen da ta yi a watan Afrilu na kashi 3.0.

Har ila yau, IMF na hasashen cewa tattalin arzikin zai ci gaba da bunƙasa da kashi 3.2 a shekarar 2026, fiye da kashi 2.7 da ta yi hasashe a baya.

Wannan sabon hasashe na nuna yuwuwar samun ci gaba a bangaren tattalin arziki a nan gaba, duk da ƙalubalen da ƴan Najeriya ke fuskanta a tattalin arziki da hauhawar farashin kayayyakin masarufi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here