Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, tare da mambobin jam’iyyar PDP sun bayyana goyon bayansu ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a yayin takarar shugaban ƙasa a babban zaben shekarar 2027.
Gwamna Adeleke ya bayyana hakan ne a wani rubutun daya wallafa a shafinsa na X a ranar Talata.
A cewar sa Jam’iyyar mu ta PDP a Osun ta amince da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tsayawa takara a 2027.