An bayar da gurbin karatu 9,469, ba bisa ka’ida ba—JAMB

0
6

Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta bayyana ta gano wasu makarantu da suka bayar da gurbin karatu ga ɗalibai 9,469 ba bisa ka’ida ba a shekarar 2024.

A cewar JAMB, wannan karɓar dalibai an yi su ne ba tare da amfani da tsarin da aka ƙirƙira domin tabbatar da gaskiya da adalci a tsarin karɓar dalibai a Najeriya.

Tsarin yana baiwa ɗalibai damar lura da matsayin shigarsu makaranta tare da tabbatar da cewa an bi duk ƙa’idoji na karɓar ɗalibai.

Makarantun da aka fi samun adadin waɗanda aka karɓa ba bisa ka’ida ba sun haɗa da,

Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote Kano – 2,215

Jami’ar Ladoke Akintola – 1,215

Jami’ar Jihar Gombe – 1,164

Jami’ar Emmanuel Alayande ta Koyar da Malamai – 761

Jami’ar Fasaha ta Tarayya Owerri – 534

Jami’ar Ambrose Alli – 514

Jami’ar Igbinedion – 365

Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Akwa Ibom – 340

JAMB ta ja kunnen makarantu da su daina karɓar ɗalibai ta hanyar da ba ta dace ba.

 Hukumar ta gargadi cewa irin wannan aiki zai iya janyo mummunan sakamako ga ɗalibai da makarantu. 

Daga ciki akwai yiwuwar hana ɗaliban da abin ya shafa halartar hidimar ƙasa ta NYSC, tare da ɗaukar matakin doka kan makarantu da mutanen da suka aikata hakan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here