Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan sabbin dokokin tsarin haraji na ƙasa a yau Alhamis, matakin da ake ganin zai kawo sauyi wajen tattara haraji da kuma inganta yanayin kasuwanci a Najeriya.
Wannan mataki ya biyo bayan cece-kuce da suka biyo bayan gabatar da dokokin a gaban majalisar dokoki, inda aka sha bayyana ra’ayoyi masu sabani dangane da tasirinsu ga ‘yan kasuwa da tattalin arzikin ƙasa.