‘Yan Majalisa  biyu sun fice daga PDP da LP zuwa APC

0
121

Wasu yan majalisar wakilai guda biyu daga PDP LP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

‘Yan majalisar da suka sauya sheƙa su ne, Hon. Peter Akpanke, mai wakiltar mazabun Obanliku/Obudu/Bekwarra a Jihar Cross River.

Sai Farfesa Paul Nnamchi, mai wakiltar mazabun Enugu East/Isi Uzo a Jihar Enugu.

Sun bayyana rikice-rikicen cikin gida a cikin jam’iyyunsu na baya da kuma buƙatar daidaita kansu da manufofi da shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya a matsayin dalilan sauya shekar da suka yi.

Da yake karanta wasikun sauya shekar a zaman majalisar, Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Abbas Tajudeen, ya taya su murna bisa matakin da suka dauka na komawa jam’iyyar APC mai mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here