Gwamnatin Najeriya ta tura dakarun sojin ta su 197 zuwa ƙasar Gambia domin gudanar da aikin tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a ƙarƙashin rundunar ECOWAS mai suna ECOMIG.
Sojojin da aka tura sun kammala horo na musamman kafin tafiya, kuma za su wakilci Najeriya a aikin wanzar da zaman lafiya wanda ƙungiyar tattalin arzikin ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ke jagoranta.
A yayin bikin yaye sojojin da aka gudanar a Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna, Shugaban Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Uwem Bassey, ya bukaci dakarun da su nuna ƙwarewa, kishin ƙasa da jarumta a yayin aiwatar da aikinsu.
Ya jaddada muhimmancin mutunta dokoki, al’adu da hakkokin bil’adama, tare da gargaɗin cewa duk wani soja da aka samu da laifi musamman kan batutuwan cin zarafin jinsi, zai fuskanci hukunci mai tsauri.
Manjo-Janar Bassey ya ce Najeriya na da dogon tarihi wajen bada gudummawa a ayyukan samar da zaman lafiya a sassa daban-daban na duniya.
Najeriya ta taka muhimmiyar rawa a rikice-rikicen da suka faru a Lebanon, Yugoslavia, Laberiya, Saliyo da Sudan, inda dakarunta suka samu yabo saboda jajircewarsu da sadaukarwa.