Sojoji sun Lalata Wurin Kera Bama-Bamai da Motocin Yaƙi Borno

0
108

Rundunar Sojin Saman Najeriya (NAF), ƙarƙashin atisayen Operation Hadin Kai, ta lalata wani wurin kera na’urorin fashewa (bama-bamai),  da lalata motocin yaƙi na ‘yan ta’adda, tare da kashe daruruwan mayaƙa a Kwaltiri, cikin yankin Tumbuktu Triangle na jihar Borno.

Wannan jawabi na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan Hulɗa da jama’a na rundunar Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar a ranar Alhamis a Abuja.

Ejodame ya bayyana cewa hare-haren saman da aka kai a ranar Laraba sun biyo bayan rahotannin sirri da suka nuna ayyukan ‘yan ta’adda a yankin.

Ya ce binciken da jiragen leƙen asiri suka yi ya tabbatar da akwai wurin kera bama-bamai da kuma wasu motoci a wurin, wanda jiragen yakin suka kai musu hari.

A cewar sa, wannan aiki ya kasance babbar illa ga ƙarfin mayaƙan, domin hare-haren sun tarwatsa tsarin jagoranci da hanyoyin jigilar kayayyaki na ‘yan ta’addan, tare da haifar da ruɗani a tsakanin su, lamarin da ya rage musu ƙwarin guiwa da kuzarin gudanar da hare-hare.

“Wannan aiki ya ƙara tabbatar da aniyar NAF na ci gaba da rage ƙarfin ‘yan ta’adda da inganta tsaro a yankin Arewa maso Gabas,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here