Yayin da a’lumma ke cigaba da yin shirye-shiryen bikin babbar Sallah Gwamnatin Kano ta bukaci mazauna jihar dasu bayar da muhimmanci wajen duba lafiya da tsaftar dabbobin da za a yi hadaya dasu domin kaucewa yaduwar cututtuka.
Jaridar Daily News 24 ta rawaito cewa wannan kiran ya fito daga ma’aikatar lafiya ta Kano, ta hannun jami’in hulÉ—a da jama’a na Ma’aikatar wato Nabilusi Abubakar K/Na’isa, cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.
Sanarwar tace kwamishinan Lafiya na Kano Dr. Abubakar Labaran Yusuf, ya jaddada cewa ya zama dole a tabbatar cewa dabbobin da za’a yanka a lokacin bikin sallah sun samu takardar tabbatar da lafiyarsu, domin kare lafiyar jama’a da hana yaduwar cututtukan da ke iya yaÉ—uwa daga dabba zuwa mutum.
Kwamishinan ya shawarci jama’a da su kula da yadda ake sarrafa nama da yadda ake dafa shi, inda yace dafa nama sosai na taimakawa wajen kashe Æ™wayoyin cuta da ka iya kasancewa a cikin sa.
Ya yi kira ga iyaye mata da masu dafa abinci da su É—auki nauyin tabbatar da tsafta wajen girki da sarrafa abinci.
Dr. Yusuf ya kuma jaddada muhimmancin wanke nama da ruwa mai tsafta kafin a dafa shi ko a ajiye shi, yana mai cewa wannan mataki ne mai sauƙi amma mai matuƙar tasiri wajen hana gurbacewar abinci da tabbatar da ingancinsa.
Ya tabbatar wa da al’umma cewa gwamnatin jihar ta tanadi isassun magunguna da kayan agajin gaggawa a cibiyoyin lafiya domin dakile duk wani matsanancin yanayi da ka iya tasowa a lokacin bikin Sallah.
A ƙarshe, ya mika sakon taya murna na bikin Eid-el-Kabir ga al’ummar Kano.