Tawagar jami’an gwamnatin Ogun ta kawo ziyarar ta’aziyyar ƴan wasan Kano

0
81

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Ogun, Noimot Salako-Oyedele, ta sauka a jihar Kano, don jajantawa al’umma rashin waɗanda suka wakilci jihar Kano a gasar wasanni ta ƙasa data gudana a jihar Ogun.

Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo, ne ya karɓi baƙuncin Noimot, da yan tawagar ta, bayan sun sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano.

Idan za’a iya tunawa dai a jiya Asabar ne motar tawagar data wakilci jihar Kano a gasar wasanni ta ƙasa da aka gudanar a jihar Ogun ta gamu da hatsari a hanyar su ta dawowa gida, wanda hakan yayi sanadiyar mutuwar mutane 22, tare da jikkata wasu da dama.

Tuni gwamnatin Kano ta sanar da bayar da tallafin Naira miliyan 1 ga iyalan kowanne daga cikin waɗanda suka rasu, tare da ayyana Litinin a matsayin ranar hutu don jimamin rasuwar ƴan tawagar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here