Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya nada Mai Martaba Sarkin Karaye, Alhaji Dr. Muhammad Mahraz Karaye, a matsayin shugaban zai jagorantar kwamitin gudanar da aikin hajjin 2025 daga jihar.
Bayanin hakan na cikin wata sanarwa da Sulaiman A. Dederi, ya fitar, inda ya bayyana cewa kwamitin zai kasance cibiyar tsarawa da sa ido kan dukkan harkokin aikin hajjin bana daga farko zuwa ƙarshe.
Gwamnan ya ce an zaɓi Sarkin Karaye don jagorantar wannan tawaga domin tabbatar da ingantaccen tsarin gudanar da aikin hajji ga alhazai ‘yan asalin jihar Kano.
Mambobin kwamitin sun haɗa da:
Hon. Sarki Aliyu Daneji, ɗan majalisar dokokin mai wakiltar ƙaramar hukumar birni
Kwamishinan Harkokin Addinai, Sheikh Tijjani Auwal
Kwamandan Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa
Sheikh Tijjani Bala Kalarawi
Sheikh Dr. Bashir Aliyu Umar
Dr. Al-Fatihi Karbullah
Alhaji Yusuf Lawan
Sheikh Isma’il Ilyasu Mangu
Sheikh Tijjani Sani Maihula
Alhaji Abdullahi Kabir Yusuf
Hajiya Aisha Munnir Matawalle
Sheikh Basheer Arabi
Sakataren kwamitin shi ne Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa.
Wasu daga cikin waɗanda aka naɗa domin gudanar da aikace-aikace sun haɗar da;
Alhaji Yusuf Aliyu Muktar
Alhaji Muhammad Ghali Muhammad
Alhaji Umar Yakubu Kabara
Alhaji Murtala Lawan Sani
Hajiya Kubura Ibrahim Dankani
Hajiya Batulu Isa Waziri
Alhaji Abdullahi Muhammad Indabawa
Alhaji Hussani Abdul Inuwa
Gwamna Yusuf ya ja hankalin mambobin kwamitin da su gudanar da aikinsu da cikakken ƙwazo, gaskiya da rikon amana, yana mai roƙon Allah yasa ayi aikin hajji karɓaɓɓe.