Shugaban ƙasa Tinubu ya dawo daga rantsar da Fafaroma
Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya dawo gida Najeriya bayan daya halarci bikin rantsar Fafaroma Leo XIV, a birnin Rome na ƙasar Italiya.
Tinubu ya samu tarba daga manyan jami’an gwamnatin tarayya da suka ƙunshi ministan Abuja, Nyeson Wike da Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume da shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.
Tinubu ya sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe dake birnin tarayya Abuja.