Boko Haram ta kashe manoma 90 a jihar Borno

0
51
Borno
Borno

Mayaƙan Boko Haram da ISWAP sun yi ajalin manoman jihar Borno 90 cikin watanni 5 suka shuɗe.

A baya-bayan nan kungiyoyin biyu suka kashe manoma kimanin 50, yawancinsu ta hanyar kisan gilla, kuma hanr yanzu an kasa dauko gawarwakin, a Kamarar Hukumar Kukawa.

Mayakan sun kuma yi garkuwa da wasu da dama baya ga wadanda suka tsallake rijiya da baya a hare-hare.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa kungiyoyin ‘yan ta’addan sun kai hare-haren ne a tsakanin watan Janairu zuwa Mayun da muke ciki.

Hari na baya-bayan nan shi ne wanda mayakan kungiyar ISWAP suka ritsa manoman da ke aiki a gonakin wake suka yi wa mutum 50 kisan gilla a yankin Karanti da ke Karamar Hukumar Kukawa a ranar Alhamis, 15 ga watan Mayu.

A gefe guda kuma, mayakan kungiyar Boko Haram da basa yin shiri da ISWAP sun kai wani hari garin Baga, inda suka yi wa masu kamun kifi da manoma kisan gilla.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here