Kabiru Alhassan Rurum ya fice daga NNPP

0
31

Kabiru Alhassan Rurum ya fice daga NNPP

Ɗan Majalisa mai wakiltar Rano, Kibiya da Bunkure, a majalisar wakilai Kabiru Alhassan Rurum, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.

Shugaban Majalisar wakilai Tajuddeen Abbas, ne ya karanta wasikar sauyin shekar Rurum a yayin a zaman majalisar.

Bayanin hakan na cikin wata sanarwar da mai taimakawa ɗan majalisar a fannin kafafen yada labarai Fatihu Yusuf Bichi, ya fitar a yau Alhamis.

Rurum dai shine shugaban kwamitin majalisar wakilai mai kula da harkokin sojojin sama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here