Jirgin farko na maniyyatan Kano ya tashi 

0
41

Mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, da sarkin Kano Muhammadu Sunusi II, sun ƙaddamar da tashin jirgin farko na maniyyata Hajjin bana daga jihar Kano a yau Laraba.

An ƙaddamar da tashin maniyyatan a filin tashi da saukar jiragen sama na Malam Aminu Kano, wanda jirgin Max Air, ya ɗauke su.

Tuni dai maniyyatan sun bar gida Najeriya, inda zasu sauka a ƙasa birnin Madina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here