Ƙarancin wutar lantarki yayi sanadiyar mutuwar marasa lafiya a wasu asibitocin arewa

0
30

Matsalar ƙarancin wutar lantarki a asibitocin Najeriya na jefa marasa lafiya cikin halin ƙunci, wanda hakan ke haddasa asarar rayukan masu jinya a wasu lokutan.

Rahoton jaridar Aminiya, ya bayyana cewar rashin wutar ya yi sanadin mutuwar jariri a cikin wata mai juna biyu, wata ta yi awa 15 tana jiran a yi mata tiyatar haihuwa, wata kuma ta mutu sakamakon dauke wuta a yayin da ake tsaka da yi mata tiyata, a Asibitin Jummai Babangida Aliyu, da ke jihar Neja.

Jaridar tace an shafe sama da kwana uku a jere babu wutar lantarki a asibitin gwamnatin, a yayin da rashin wuta da yanayi na tsananin zafi ya tilasta wa ’yan uwan majinyata amfani da fankoki masu amfani da caji domin samun iska a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke Jihar kano.

Sai dai a cikin wannan hali, Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya sanar da shirin sake kara kudin wutar, bisa hujjar cewa gwamnati ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin lantarki ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here