Najeriya ce kasar da tafi kowacce yawan yara masu fama da rashin abinci mai gina jiki—UNICEF

0
31

Asusun tallafawa ƙananun yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (Unicef) ya bayyana cewa Najeriya ce ke da mafi yawan yara masu fama da matsanancin ƙarancin abincin masu gina jiki a nahiyar Afirka.

A cewar sanarwar da asusun ya wallafa a shafinsa na intanet ranar Talata, daga cikin yara 10 da ke fama da wannan matsala biyu ne kawai ke samun magani.

Asusun ya bayyana cewa kimanin yara miliyan biyu ne a Najeriya ke fama da mmatsalar ta tamowa, inda hakan ya sa Najeriya ke da mafi yawan yaran da ba su girma yadda ya kamata kuma ta biyu a duniya, da kashi 32 cikin 100 na yara ‘yan ƙasa da shekara biyar.

Hakazalika, Unicef ya ce kashi 7 cikin 100 na mata masu haihuwa a Najeriya na fama da matsanancin ƙarancin abinci.

Asusun ya nuna damuwa kan yadda ƙarancin abinci ke haddasa kashi 45 cikin 100 na mace-macen yara ‘yan ƙasa da shekara biyar tare da barazana ga lafiyar jama’a da tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here