Gwamnatin Edo tayi ƙarin mafi ƙarancin albashin ma’aikata

0
39

Gwamnan Edo, Monday Okpebholo, ya amince a riƙa biyan ma’aikatan jihar Naira dubu 75 a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Gwamna Monday Okpebholo, ne ya sanar da hakan da bakin sa yayin bikin ranar ma’aikatan daya gudana a filin wasa na Ogbemudia, dake Benin, a yau Alhamis.

Tunda farko dai kungiyar ƙwadago ta NLC tace Naira 70,000 ta yi kaɗan a matsayin mafi ƙarancin albashi a Najeriya.

Gwamnan, yace anyi ƙarin albashin don ƙarfafa gwuiwar ma’aikata da kuma yaba musu.

Ya kuma roki ma’aikatan jihar dasu zamo masu sadaukarwa don inganta harkokin aikin gwamnati da Edo, baki ɗaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here