An kama waɗanda suka kashe jami’in KAROTA da wuƙa

0
71

Hukumar Kula da zirga Zirgar ababen hawa ta jihar kano KAROTA, ta sanar da kama waɗanda suka kashe jami’in ta da wuƙa a lokacin da yake bakin aiki.

Daga cikin wadanda aka Kama bisa zargin hallaka jami’in akwai direban wata babbar mota da yaron sa, sai kuma wani jami’in Soja.

Shugaban hukumar Injiniya Faisal Mahmoud, ya ce zasu yi bakin kokari wajen tabbatar da adalci ga jami’in da aka hallaka musu.

Idan za’a iya tunawa a wannan mako ne aka samu labarin cewa wasu mutane sun yiwa jami’in KAROTA kisan gilla lokacin da yake bakin aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here