Gwamnatin Borno zata  gyara rijiyoyin burtsatse da Naira miliyan 850

0
25

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum, ya amince a fitar da kuɗaɗen da yawan su yakai Naira miliyan 850, da za’a yi amfani dasu wajen gyara rijiyoyin burtsatse a Maiduguri da kewaye.

Yunkurin baya rasa nasaba da kokarin magance matsalolin rashin ruwan sha da ake fama da ita a Maiduguri biyo bayan ambaliyar ruwan da birnin ya fuskanta a ranar 10 ga watan Satumba na shekarar 2024.

Shugaban hukumar samar da ruwan sha a ƙauyukan Borno Dr. Muhammad Musa Aliyu, ne ya sanar da hakan ga manema labarai a birnin Maiduguri.

Yace gwamna Zulum ya bayar da umurnin fitar da kuɗin don siyo duk wasu abubuwan da za’a yi amfani da su wajen gyara rijiyoyin, a Maiduguri da kewaye.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here