Ƴan bindiga sun ta’adda sun tarwatsa gada a jihar Yobe

0
98

Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gadar da ta haɗa garin Ngirbuwa da garin Goneri a ƙaramar hukumar Gujiba da ke jihar Yobe.

Tarwatsa gadar yazo mako ɗaya bayan da ‘yan ta’addan suka lalata gadar Mandafuna da ta haɗa garin Biu da Damboa a Jihar Borno.

Wata majiya ta shaidawa Zagazola Makama, cewa harin ya afku da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar ranar Alhamis ɗin da ta gabata, ta hanyar amfani da wani bam wajen lalata sauran sassan gadar.

Harin ya kawo cikas ga zirga-zirga tsakanin al’ummomin biyu da ma sauran su, saboda gadar na kan hanyar Katarko zuwa garin Goneri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here