Lakurawa sun kashe hallaka ƴan Bijilanti a jihar Kebbi

0
83

An gabatar da jana’izar mutum shida daga cikin mutane Goma sha uku da lakurawa suka kashe a garin Morai dake mazabar Yola, a karamar hukumar mulki Augie jihar Kebbi.

Lamarin ya faru bayan da ‘yan sa-kai suka yi kokarin hana Lakurawa daukar dabbobin mutanen yankin.

Gwamna Nasir Idris na jihar ta Kebbi a ranar Lahadi ya yi allawadai da harin wanda ya ce ya girgiza shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here