Gas yayi bindiga a Lagos, har ya jikkata mutane da dama

0
66

Fashewar Gas mai ƙarfi tayi sanadiyar jikkatar mutane 15, ta hanyar jin munanan rauni, biyo bayan faruwar lamarin a yankin Ijora Badia dake karamar hukumar Apapa Iganmu.

Lamarin dai ya faru a yammacin jiya Lahadi.

Fashewar ta faru da misalin karfe 4:10, na yamma lokacin da wata tukunyar gas mai nauyin kilo 25 tayi bindiga, a wani shagon siyar da gas.

Shago ya kasance a jikin wani gida mai mazaunin mutane 15, da kuma shaguna 7.

Shugabar hukumar bada agajin gaggawa akan faruwar gobara Margaret Adeseye, ta tabbatar da afkuwar lamarin a ranar Lahadi.

Ta kuma ɗora alhakin faruwar fashewar Gas din akan rashin bayar da kulawa yayin ma’amala da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here