Kungiyar dattawan arewa ta nemi Tinubu ya dawo da gwamna Fubara kan muƙamin sa cikin hanzari.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar Abubakar Jika Jiddere ya fitar, NEF, ta ce abubuwan da suka faru a Rivers ba su kai girman da shugaban kasa zai ayyana dokar ta-baci tare da sauke gwamnan na wucin gadi ba.