Tinubu ya aikata abinda ya ƙalubalanci tsaffin shugabannin Najeriya dashi

0
34
Bola Ahmed Tinubu
Bola Ahmed Tinubu

Shugaban ƙasa Tinubu ya aikata irin abinda ya ƙalubalanci tsaffin shugabannin Najeriya Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan, da aikata dangane da sanya dokar ta ɓaci a jihohi.

Idan za’a iya tunawa a shekarar 2004, ya ƙalubalanci Obasanjo kan yadda ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar Filato a ranar 18 ga watan Mayu.

Bayan haka ya kalubalen tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, yayin da ya ayyana dokar ta ɓaci a jihohin Adamawa, Borno da Yobe, a ranar 14 ga watan Mayu na shekarar 2013.

Sai gashi a jiya 18 ga watan Maris, Tinubu ya saka dokar ta ɓaci a jihar Rivers, tare da dakatar da gwamnan jihar zaɓaɓɓe Siminalaya Fubara, da mataimakiyar sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here