Amurka ta kori jakadan Afrika ta Kudu

0
52

Idan za’a iya tunawa dai rikicin diflomasiyya ya kunno tsakanin kasashen Afrika ta Kudu da Amurka, inda shugaba Trump, ya zargi gwamnatin Ramaphosa da kwace kadarorin Amurkawan dake zaune a Afrika ta Kudu.

Kadarorin sun kunshi gonaki da filaye, sai dai gwamnatin Afrika ta Kudu ta musanta zargin da Amurka tayi.

Ko a kwanakin baya sai da shugaban Amurka Donald Trump, yace zai bawa manoman Afrika ta Kudu damar zama a Amurka in har tsoron zaman kasar saboda barazanar gwamnati.

Wannan rikicin shine dalilin korar jakadan bayan Amurka ta zarge shi da kalubalantar Trump.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here